1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaGabas ta Tsakiya

Isra'ila ta ce ta kashe kwamandojin Hezbollah guda goma

Mouhamadou Awal Balarabe
September 20, 2024

Hare-haren da sojojin Isra'ila suka kai Beirut da kan iyakar Lebanon ya yi sanadi mutuwar Ibrahim Aqil na rundunar Al-Radwan da wasu kwamandojin Hezbollah, a cewar rundunar sojin Isra'ila

https://p.dw.com/p/4kv5a
Hare-haren Isra'ila a Lebanon sun lalata gine-gine tare da salwantar da rayuka
Hare-haren Isra'ila a Lebanon sun lalata gine-gine tare da salwantar da rayukaHoto: Anwar Amro/AFP/Getty Images

Kakakin rundunar Isra'ila Rear Admiral Daniel Hagari ya ce harin ya kashe fararen hula da Ibrahim Aqil da ke zama kwamandan rundunar Al-Radwan, wanda Amurka ke nema sakamakon zarginsa da marar hannu a harin Beirut a shekarar 1983. Amma bayan hare-haren da sojojin Isra'ila suka kai Beirut wanda suka yi kashe kwamandojin Hesbollah, kungiyar ta dauki alhakin harba wa isar'ila rokoki 140 tare da alkawarin daukar fansa.

Krin bayani: Zaman tankiya kan iyakar Lebanon da Isra'ila

Majalisar Dinkin Duniya ta nuna damuwa kan halin da ake ciki a Lebanon musamman dangane da hare-haren Isra'ila ke kaiwa, inda ta yi kira ga bangarorin biyu da suka kai zuciya nesa. Ita ma Kungiyar Hamas da ke yaki da Isra'ila a zirin Gaza, ta yi Allah wadai da harin da Isra'ila ta kai a birnin Beirut, tana mai danganta kashe daya daga cikin shugabannin Hezbollah na kasar Labanon da mummunan tashin hankali.