1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Tuhumar tsohon firaministan Pakistan

Suleiman Babayo ZMA
August 22, 2022

An shiga dambaruwar siyasa kan batun tuhumar tsohon Firaminista Imran Khan na Pakistan wadda gwamnati take zargi da zagon kasa.

https://p.dw.com/p/4Frsq
Pakistan Imran Khan, Rede in Lahore
Hoto: K.M. Chaudary/AP Photo/picture alliance

'Yan adawa na kasar Pakistan sun yi gargadi kan yuwuwar kama tsohon Firaminista Imran Khan wanda ake neman tuhuma karkashin dokokin yaki da ta'addanci.

Tun bayan tunbuke shi kan madafun iko a watan Afrilu, tsohon Firaminista Imran Khan yake gangami a sassan kasar inda ake ganin yana zagon kasa ga gwamnatin Firaminista Shehbaz Sharif.

A wannan Litinin akwai akwai kimanin magoyan bayan tsohon firaministan 500 suka yi gangami a gefen gidansa da ke unguwar masu hannu da shuni a Islamabad babban birnin kasar ta Pakistan.

Yanzu haka 'yan sanda sun shigar da tuhumar bisa ta'addanci a kan tsohon tsohon Firaminista Imran Khan lamarin da ya kara zaman tankiya na siyasa a kasar.