1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An kafa gwamnatin wucin gadi a Afghanistan

Abdoulaye Mamane Amadou
September 7, 2021

Kungiyar Taliban ta sanar da Mohammad Hassan Akhund a matsayin wanda zai ja ragamar sabuwar gwamnatin wucin gadi da ta kafa, makwanni uku bayan da ta kwace iko daga hannun gwamnatin farar hulla a Afghanistan.

https://p.dw.com/p/402ou
Afghanistan | Videostatement der Taliban - Mullah Baradar Akhund soll Taliban leiten
Hoto: SOCIAL MEDIA/REUTERS

A wata ganawa da manema labarai a wannan yammaci a birnin Kabul, kakakin kungiyar Zabihullah Mujahid ya kuma bayyana cewa an nada Mullah Abdul Ghani Baradar a matsayin mataimakin firaminista haka kuma Maulawi Mohammad Yaqoob Mujahid zai rike mukamin ma'aikatar tsaron kasa, kana kuma Alhaj Mullah Serajuddin Haqqani zai kasance ministan cikin gida a yayin da Maulawi Amir Khan Muttaqi kuwa zai jagoranci ma'aikatar harkokin waje.

Kungiyar ta girmama tsoffin jiga-jiganta da suka yi gwagwarmaya ta tsawon shekaru 20 bayan tunbukesu daga jagorancin Afghanistan ta hanyar nada wasu daga cikinsu a manyan mukamai, ciki har da shugaban gwamnati Mohammad Hassan Akhund da ya kasance tsohon gwamna a Kabul yayin mulkin kungiyar, haka shima Mullah Abdul Ghani Baradar, na daga cikin na gaba gaba da suka jagopranci tattaunawar ficewar Amirka daga Afghanistan.